Jaridar Hausa - Labaran Cigaban Alumma a Dukkan Fannoni

Muhimman Abubuwa Da Ya Kamata A Sani Game Da Ganduje

An haifi Abdullahi Umar a ƙauyen Ganduje da ke cikin ƙaramar hukumar Dawakin Tofa ta jihar Kano a 1949.

Ya fara karatun Ƙur’ani da Islamiyya a ƙauyensu, inda ya samu ilimin addini. Ya shiga firamare ta Dawakin Tofa daga 1956 zuwa 1963.

Ganduje ya fara makarantar sakandiren Birnin Kudu a 1964 inda ya kammala a 1968.

Ya shiga makarantar horar da malamai da ke Kano tsakanin 1969 zuwa 1972.

Tsohon gwamnan jihar Kanon ya samu digirinsa na farko a fannin ilmin malanta a Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zaria cikin jihar Kaduna a 1975.

A 1979 ne kuma ya kammala digirinsa na biyu a Jami’ar Bayero ta Kano, sannan ya sake komawa Jami’ar Ahmadu Bello daga 1984 zuwa 1985 don karanta fannin gudanar da harkokin gwamnati.

A 1993 ne ya samu digirin-digirgir daga Jami’ar Ibadan.

Siyasarsa

Ganduje ya shiga jam’iyyar NPN a jamhuriyya ta biyu sannan ya zama mataimakin sakatare na jihar Kano daga 1979 zuwa 1980.

Ya tsaya takarar ɗan majalisar wakilai a 1979 ƙarƙashin jam’iyyar NPN, amma bai yi nasara ba.

A 1998, ya shiga PDP inda ya nemi jam’iyyar ta tsayar da shi takarar gwamna, amma bai yi nasara ba, maimakon haka sai ta tsayar da Rabi’u Musa Kwankwaso.

Amma aka zaɓi Ganduje a matsayin mataimakin Kwankwaso tsakanin 1999 da 2003, sun sake cin zaɓen gwamna da mataimakin gwamna a Kano a shekara ta 2011 zuwa 2015.

A 2015 ne kuma, aka zaɓi Dakta Abdullahi Umar Ganduje matsayin gwamnan Kano, inda ya yi wa’adin mulki biyu daga 2015 zuwa 2023.

BBC HAUSA