Jaridar Hausa - Labaran Cigaban Alumma a Dukkan Fannoni

Ɗan Majalissar Wakilai Zai Raba Kayan Abinci Ga Zawara 2,000

Ɗan Majalissar Wakilai mai wakiltar Darazo da Ganjuwa daga Jihar Bauchi, Mansur Manu Soro ya ce, zai samar da kayan abinci kyauta ga zawara 2,000 a mazaɓarsa.

Ɗan majalissar ya bayyana hakan ne ga jaridar DAILY TRUST a jiya Laraba, a wata tattaunawa da suka yi.

Ya ce, “Bayan cire tallafin man fetur, ƴan Najeriya sun tsinci kansu cikin mawuyacin hali da ke ƙara tsanani ga matsalolin rayuwarsu.

“Saboda haka, a kan wannan yanayi ne na yanke shawarar samar da tallafin abinci ga mata 2,000 musamman ma zawarawa.