Jaridar Hausa - Labaran Cigaban Alumma a Dukkan Fannoni

Likitoci Sun Janye Yajin Aikin Sai Baba Ta Gani Da Suka Yi

Ƙungiyar Likitoci Masu Neman Ƙwarewa ta Najeriya, NARD, ta janye yajin aikin sai baba ta gani da take yi a duk faɗin ƙasa, inda likitocin suka dawo aiki a yau Asabar.

Shugaban Ƙungiyar na Ƙasa, Innocent Orji ne ya tabbatar da hakan a jiya Juma’a da yamma.

Ya ce, sun janye yajin aikin ne da nufin dawowa aiki a yau Asabar da misalin ƙarfe 8 na safe, sannan kuma zasu duba irin nasarar da suka samu a sati biyun da suka ɗebe suna daka yajin.

Wannan dai na zuwa ne ƴan kwanaki kaɗan bayan likitocin sun dakatar da yin zanga-zanga a duk faɗin ƙasa domin takurawa gwamnati kan buƙatunsu.

Shugaban na NARD ya bayyana cewa, likitocin na da buƙatu takwas ne a wajen gwamnati waɗanda a cikinsu har da buƙatar ɗaukar sabbin likitocin da zasu cike guraben waɗanda suka bar aikin, ko kuma suka mutu.

KARANTA WANNAN: JIGAWA: Gwamna Namadi Ya Cire Shugabannin Asibitin Gumel

Ya ce, likitoci na shan wahala matuƙa saboda ƙarancinsu na shafar aiyukansu na bayar da temakon lafiya a Najeriya, inda ya jaddada cewar, kowa ya san cewar hakan gaskiya ne.

Ya ƙara da cewa, Gwamnatin Tarayya tun a watan Fabarairu da ya gabata ne ta samar da kwamiti da ya fito da tsare-tsaren yanda za a yi, amma har kawo wannan lokaci ba a bayyana tsare-tsaren ba.

Ya kuma bayyana cewa, har kawo wannan lokacin da suka janye yajin aikin, gwamnati ba ta biya buƙatun likitocin ba.

Tun a baya dai, shugabannin ƙungiyar NARD sun gana da sanatoci, ƙarƙashin jagorancin Shugaban Majalissar Sanatocin, Godswill Akpabio kan buƙatun likitocin.

A ranar 25 ga watan Yulin da ya gabata ne likitocin suka shiga yajin aikin sai baba ta gani, suna buƙatar gwamnati ta biya musu buƙatunsu ciki har da ƙarin albashi.