Afenifere Ta Zargi Tinubu Da Aiwatar Da Mulkin Kama Karya

Ƙungiyar Afenifere ta zargi gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da neman koma wa salon mulkin kama-karya irin na Janar Sani Abacha.

Ƙungiyar ta bayyana shirinta na kafa wata ƙungiyar siyasa don ƙwace mulki daga hannun gwamnati mai ci a zaben 2027.

Sakataren Yaɗa Labarai na Afenifere, Justice Faloye, ya yi wannan tsokaci ne a wata hira da aka yi da shi a wata kafar talabijin a Lagos.

Faloye ya bayyana mulkin Tinubu tun bayan hawansa kan mulki a shekarar 2023 a matsayin gazawa mai girma, inda yake cin zarafin wadanda suka saɓa masa a ra’ayi.

Ya ƙara da cewa gwamnatin na cin mutuncin shugaban ƙungiyar ƙwadago da kuma tsare mutane saboda shiga zanga-zangar ƙin jinin yunwar da gwamnatin Tinubu da jawowa ƴan Najeriya.

Faloye ya yi zargin cewa an hana ƴancin zanga-zanga a ƙarƙashin mulkin Tinubu, inda masu zanga-zanga suke fuskantar tsarewa ba bisa ƙa’ida ba.

Har ila yau, ya ce al’ummomin duniya sun yi Allah wadai da mulkin Tinubu bisa zargin kama mutanen da ke yin zanga-zanga cikin lumana a cikin tsarin dimokaraɗiyya.

Afenifere ta yi kira ga Shugaba Tinubu da ya saurari shawarar Farfesa Wole Soyinka kan gujewa kama-karya a Najeriya.

Ƙungiyar ta yi gargaɗin cewa, idan ba a ɗauki mataki ba, Najeriya na iya komawa zamanin kama-karya irin na mulkin soja.

A ƙarshe, Faloye ya bayyana cewa Afenifere na duba yiwuwar kafa wata jam’iyyar siyasa don tabbatar da gaskiya da adalci a Najeriya.

Comments (0)
Add Comment