Dantata Da Dangote Sun Bayar Da Gudunmawar Naira Biliyan 2.5 Ga Waɗanda Ambaliyar Ruwa Ta Yi Wa Ta’adi A Borno

Aminu Dantata da Aliko Dangote sun bayar da tallafin naira biliyan 2.5 ga waɗanda ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri, babban birnin Jihar Borno.

Alhaji Aminu Dantata ya ba da gudunmuwar naira biliyan 1.5 ne lokacin da ya jagoranci tawagar daga Kano zuwa gidan gwamnati a Maiduguri ranar Talata don jajantawa mutanen da abin ya shafa.

Ya miƙa saƙon ta’aziyyarsa ga Gwamna Babagana Zulum, gwamnatin jihar, da al’ummar Borno, musamman dangin da suka rasa ƴan’uwansu a ambaliyar.

Dantata ya bayyana damuwarsa game da matsalar tattalin arziƙin Najeriya, yana mai kira ga shugabanni su tuba su ji tsoron Allah.

Ya yi addu’ar samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a Jihar Borno da Najeriya baki daya.

A jawabinsa, Gwamna Zulum ya nuna godiyarsa ga Dantata, yana mai cewa ziyarar ta zama wata salama da samun goyon baya a lokacin jarrabawa.

Haka kuma, Dantata ya bi sahun ɗansa, Alhaji Aliko Dangote, wanda shima ya bayar da gudunmuwar naira biliyan 1 don tallafawa wadanda ambaliyar ruwa ta shafa.

DangoteDantata
Comments (0)
Add Comment