EU Ta Dakatar Da Tallafin Da Ta Ke Bai Wa Jamhuriyar Nijar

Ƙungiyar Tarayyar Turai, EU, ta ce ta dakatar da duk wani tallafi na kuɗi da take bai wa Nijar tare da yanke duk wata hulɗa a kan abin da ya shafi tsaro a tsakaninta da ita,  biyo bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a ƙasar.

Jagoran manunfofin hulɗa da ƙasashe na EU, Josep Borrell ne  ya  bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar.

RFI Hausa ta rawaito cewa, waɗanda suka yi juyin Mulki a Nijar sun ayyana Janar Abdourahamane Tchiani a matsayin shugaban ƙasa a ranar Juma’a, bayan da suka wancakalar da zaɓaɓɓen shugaban ƙasa, Mohammed Bazoum.

Tarayyar Turai,  Amurka, ECOWAS, AU da sauran ƙasashen duniya sun yi kira da a saki shugaba Bazoum ba tare da gindaya wasu sharuɗa ba, sannan a maido da mulkin demokaraɗiyya a ƙasar.

RFI Hausa ta ce, Nijar ce kasar da ta fi samun tallafi  daga ƙasashen Turai, kuma babbar abokiyar aikin EU a wajen yaƙi da bakin haure da ke bi ta sahara zuwa nahiyar Turai.

Ƙungiyar Tarayyar Turai ta wallaafa a shafinta na intanet cewa, ta kasafta kuɗin da ya kai Yuro miliyan 503 tun daga shekarar 2021 don bunƙasa sha’anin mulki da ilimi a Jamhuriyar Nijar.

EUJuyin MulkiNijar
Comments (0)
Add Comment