Jawabin Ganduje Na Kama Aiki

Sabon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya ce zai fara aiki ba tare da sanyin jiki ba don tabbatar da nasarar jam’iyyar mai mulki a zaɓukan gwamna na ranar 11 ga watan Nuwamba a jihohin Imo da Kogi da kuma Bayelsa.

Tsohon gwamnan Kano, Ganduje ya yi wannan jawabi ne jim kaɗan bayan tabbatar da shi a matsayin shugaban APC na ƙasa a yau Alhamis.

Ganduje ya kuma yaba wa Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, kuma ya yi alƙawarin cewa a zamanin mulkinsa zai tabbatar da ganin demokaraɗiyya ta yi tasiri a cikin gida.

Ya kuma yi alƙawarin cewa zai tabbatar da rijistar gaskiya ta ƴaƴan jam’iyyar APC, kuma zai mayar da hankali ga sha’anin gudanar da zaɓe da kuma sulhunta rikice-rikicen jam’iyyar.

A cewarsa, sabon shugabancinsa zai samar da yanayi na bai ɗaya ga dukkan ƴaƴan jam’iyyar a lokacin zaɓukan fitar da gwani.

Abdullahi Umar GandujeAPC
Comments (0)
Add Comment