Kashim Shettima Ya Yi Gargaɗi Kan Wulaƙanta Kuɗaɗen Ƙananan Hukumomi

Matimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima ya bayyana cewar, ƴancin ƙananan hukumomi zai magance matsalolin kuɗaɗe da ke jawo tarnaƙi ga cigaban ilimi a matakin farko a Najeriya.

Shettima ya ƙara da cewa, hukuncin Kotun Ƙoli na kwanan nan da ya bai wa ƙananan hukumomi cikakken ƴancin tasarrufi da kuɗaɗensu zai bunƙasa harkokin ilimi matakin farko a Najeriya.

Mataimakin Shugaban Ƙasar wanda ya kuma yi gargaɗi kan wulaƙanta ƴancin ƙananan hukumomi, ya bayyana hakan ne a wajen taron ƙaddamar da littafi mai taken ‘Navigating the Politics of Universal Education Policies in Nigeria’, wanda tsohon mataimakin gwamnan Jihar Ekiti, Modupe Adelabu ya rubuta aka kuma gabatar a Abuja yau Alhamis.

Shettima ya bayyana cewar, ƴancin ƙananan hukumomi, waɗanda ke da alhakin tafiyar da harkokin ilimi a matakin farko a Najeriya, zai magance matsalolin da ke kawo tarnaƙi wajen cimma manufar gwamnati a harkar ilimi.

Ya ƙara da cewa, sauye-sauyen da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ke ƙirƙirowa zasu magance matsalolin ƙarancin kuɗaɗe da wadatar manufofin da ke kawowa tafiyar ilimi a matakin farko a tarnaki.

Kashim Shettima
Comments (0)
Add Comment