NDLEA Ta Kara Wa’adin Daukar Sabbin Ma’aikatan Da Take Yi

Shugaban Hukumar Hana Sha da Fatucin Miyagun Kwayoyi, NDLEA, Buba Marwa, ya amince da kara wa’adin sati guda kafin a rufe shafin daukar sabbin ma’aikata na hukumar.

Buba Marwa ya bayyana hakan ne a sanarwar da Daraktan Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a na hukumar, Femi Babafemi ya fitar a jiya Alhamis a Abuja.

Sanarwar ta bayyana cewa, an yi karin ne domin bayar da dama ga masu neman aikin wadanda suka sami tasgaro a kokarinsu na cike neman aikin.

An dai bude shafin daukar sabbin ma’aikatan ne a ranar Lahadi, 12 ga watan Maris, inda aka tsara rufe shi a gobe Asabar, 8 ga watan Afirilu, 2023.

To amma yanzu da karin sati gudan da NDLEA ta yi, za a rufe shafin daukar ma’aikatan ne da misalin karfe 11:59 na daren ranar 17 ga watan Afirilu, 2023.

NAN

Daukar Ma'aikataNDLEA
Comments (0)
Add Comment