TANTANCE MINISTOCI: Ministoci 14 Da Sanatoci Ke Tantancewa A Yau

Waɗanda Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ke son naɗawa ministoci su 14 ne cikin 28 suka je Majalissar Dattawa a yau domin a tantance su.

A makon da ya gabata ne ranar Alhamis, Shugaban Majalissar Dattawa Godswill Akpabio ya bayyana sunayen mutane 28 da Shugaban Ƙasa ke son naɗawa ministoci.

Waɗanda suka je Majalissar Dattawan a yau sune:

  1. David Umahi (Ebonyi);
  2. Adebayo Olawale Edun (Ogun);
  3. Nasir El-rufai CON (Kaduna);
  4. Ahmed Musa Dangiwa (Katsina)
  5. Chief Uche Geoffrey Nnaji (Enugu);
  6. Stella Okotete (Delta);
  7. Dele Alake (Ekiti);
  8. Adebayo Adelabu (Oyo);
  9. Muhammad Idris (Niger);
  10. Professor Ali Pate (Bauchi);
  11. Doris Anite Uzoka (Imo);
  12. Lateef Fagbemi SAN (Kwara);
  13. Hon. Ekperikpe Ekpo (Akwa Ibom);
  14. Barr Hannatu Musawa (Katsina).
Tantance Ministoci
Comments (0)
Add Comment