Jaridar Hausa - Labaran Cigaban Alumma a Dukkan Fannoni

Bin Hukuncin Kotun Ƙoli Kan Ƙananan Hukumomi Dole Ne, In Ji Wani Gwamna

Gwamnan Jihar Anambra, Charles Soludo ya ce, gwamnoni zasu yi duba ga hukuncin Kotun Ƙoli wanda ya bai wa ƙananan hukumomi ƴancin tasarrufi da kuɗaɗensu.

Soludo ya bayyana hakan ne a jiya Alhamis bayan ganawa da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, inda ya kuma bayyana hukuncin Kotun Ƙolin a matsayin babban hukunci.

Ya ce, Kotun Ƙoli ita ce ƙarshe wajen fassara doka, saboda haka duk lokacin da ta bayyana hukunci to ya tabbata.

Soludo ya kuma ƙara da cewa, a daren na jiya, gwamnoni zasu zauna domin tattauna yanda zasu tafiyar da sabon tsarin, inda ya kuma jaddada cewa, hukuncin Kotun Ƙolin zai bayar da damar aiwatar da adalci.