Sign in
Sign in
Recover your password.
A password will be e-mailed to you.
Browsing Category
Babban Labari
Za A Cigaba Da Dambarwa Tsakanin Ƴanƙwadago Da Gwamnati Ranar Talata Kan Mafi Ƙarancin Albashi
Tattaunawa kan mafi ƙarancin albashi a Najeriya zata cigaba a ranar Talata mai zuwa a daidai lokacin da ake cigaba da musayen maganganu tsakanin jami’an gwamnati kan abun da ya faru a farkon makon nan inda gwamnati ta nuna zata bayar da!-->…
Babu Buƙatar Najeriya Ta Ƙara Shigowa Da Man Fetur Daga Wata Mai Zuwa, In Ji Dangote
Wanda ya fi kowa kuɗi a Afirka kuma Shugaban Rukunin Kamfanonin Ɗangote, Aliko Dangote ya bayyana tabbatuwar shirye-shiryen Matatar Dangote da zasu kai Najeriya ga dena shigowa da tattaccen manfetur daga wata mai zuwa.
Dangote ya kuma!-->!-->!-->…
Najeriya Zata Karɓi Bashin Naira Tiriliyan 3.2 Daga Bankin Duniya A Ranar 13 Ga Yuni
Gwamnatin Tarayya ta shirya domin karɓar sabon bashi daga Bankin Duniya mai yawan adadin dala biliyan 2.25 daidai da naira tiriliyan 3.2 a ranar 13 ga watan Yuni, 2024.
Najeriyar zata karɓi waɗannan maƙudan kuɗaɗe ne saboda wasu manyan!-->!-->!-->…
Shugaba Tinubu Ya Ce CBN Ya Dakatar Da Maganar Cirar Harajin Kula Da Intanet Kan Asusun Mutane
Wasu majiyoyi da ke da kusanci da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu sun bayyana cewar shugaban ya umarci Babban Bankin Najeriya, CBN da ya dakatar da batun cirar harajin bayar da tsaron intanet ga asusun bankunan ƴan Najeriya.
Majiyoyin!-->!-->!-->…
Yanzu Mu Muke Da Cikakken Iko Da Jihar Rivers – PDP
Jam’iyyar Peoples Democratic Party, PDP ta bayyana cewar ita ke da cikakken iko da Jihar Rivers, inda tai alfaharin cewa, Gwamnan jihar Siminalayi Fubara da jam’iyyar ke riƙe da madafun ikon siyasar jihar.
A wata sanarwa da Sakataren!-->!-->!-->…
Ba Zai Yiwu Ka Ƙaƙabawa Mutane Haraji Ba Tare Da Ƙara Musu Kuɗin Da Suke Samu Ba – Ndume
Sanata Ali Ndume ya kushe batun sabon haraji na kula da hadahadar banki ta intanet, inda ya ce, rashin dacewa ne gwamnati ta cigaba da cajar ‘yan ƙasa haraje-haraje ba tare da ta yi wani abu da zai ƙara musu kuɗin shigar da suke samu ba.
!-->!-->…
Tsarin Shugaban Ƙasa Ba Shi Da Amfani A Najeriya, A Koma Tsarin Firaminista, In Ji Wani Ɗan…
Wani ɗan Majalissar Wakilai mai suna Abdussamad Dasuki ya ce, tsarin da ake kai na shugaba mai cikakken iko a Najeriya ba ya temakon Najeriya, ya kamata a yi watsi da shi a dawo tsarin firaminista irin wanda aka yi a jamhuriya ta farko.
!-->!-->!-->…
Gwamnatin Tarayya Zata Sauƙaƙa Hanyar Samun Asusun Bankuna Ga Waɗanda Ba Su Da Su
Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana tsare-tsaren gwamnantin tarayya domin rage talauci da matsalar tsaro a faɗin ƙasa ta hanyar shigar da ƴan Najeriya cikin harkokin samun kuɗaɗe.
Fadar ta bayyana cewar akwai muhimman tattaunawa da ake yi!-->!-->!-->…
Rikicin Cikin Gidan Da Ke APC Da PDP Ya Fi Na Labour Party – Peter Obi
Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party a zaɓen 2023, Peter Obi a jiya Laraba ya bayyana cewar jam’iyyarsu zata magance matsalolinta na cikin gida tare da samun ƙarin ƙarfi.
Peter Obi wanda yake jawabi ga manema labarai Ya!-->!-->!-->…
Yahaya Bello Ya Yi Amfani Da Sama Da Dala 720,000 Na Jiha Wajen Biyan Kudin Makarantar Ɗansa
Shuagaban Hukumar EFCC, Oala Olukayode ya bayyana cewar, tsohon gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello ya fitar da kuɗi kimanin dala dubu 720,000 daga asusun gwamnatin jihar domin biya wa ɗansa kuɗin makaranta na shekaru masu zuwa.
A lokacin!-->!-->!-->…
Ganduje Na Tsaka Mai Wuya, Sabbin Shugabannin Mazaɓarsa Sun Ƙara Dakatar Da Shi Daga APC
Rikicin da ya dabaibaye jam’iyya mai mulki, All Progressive Congress, APC a Jihar Kano ya ƙara ɗaukar sabon salo, inda sabbin waɗanda suka bayyana a matsayin shugabannin Mazaɓar Ganduje suka fitar da sabuwar sanarwar dakatara da Shugaban!-->…
Litar Man Fetur Zata Dawo Naira 500 Idan Matatar Mai Ta Port Harcourt Ta Fara Aiki A Kwanannan
A daidai lokacin da ma’aikatan matatar mai ta Port Harcourt ke rige-rige wajen ganin sun kammala aikin daidaita matatar domin fara fitar da tataccen mai, dillalan man fetur na shiryawa domin fara saro man fetur daga matatar.
A ranar!-->!-->!-->…
An Yi Kira Ga JAMB Da Ta Sauƙaƙa Hanyar Yin Regularization Ga Masu Cike DE
Hukumar Shiraya Jarabawar Share Fagen Shiga Jami’a, JAMB ta ce duk dalibin da ya zaɓi ya sami addmission ba ta ingantacciyar hanya ba zai fuskanci.
Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da JAMB ke jaddada cewar, duk wani admission na shiga!-->!-->!-->…
Gwamnatin Kano Ta Maka Ganduje, Ɗansa Da Matarsa A Kotu Kan Zargin Badaƙala Da Kuɗaɗe
Gwamnatin Jihar Kano ta maka tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje da matarsa Hafsat Umar da ɗansa Umar Abdullahi Umar da wasu mutane biyar a kotu kan zarge-zarge guda takwas da suke da alaƙa da cinhanci da rashawa, badaƙala da!-->…
NATO Na Bikin Cika Shekaru 75 Da Kafuwa
Ministocin ƙasashen waje na rundunar NATO wadda aka kafa a shekarar 1949 domin magance barazanar sojojin rusashshiyar Tarayyar Sobiyat ga kasashen Turai sun taru domin murnar cikar rundunar shekaru 75 da kafuwa.
Bikin dai ya gudana ne!-->!-->!-->…
Shugaban Miyatti Allah Ya Ce Ba Shi Da Wata Alaƙa Da Ta’addanci
Shugaban Miyatti Allah Kautal Hore, Alhaji Bello Bodejo, wanda ke fuskantar tuhume-tuhumen ta’addanci ya buƙaci kotu da ta bayar da belinsa, inda ya ce ba shi da wani tarihi na aikata ta’addanci.
Bodejo wanda ke fuskantar tuhuma a!-->!-->!-->…
Malam Adamu Foundation Zata Ɗau Nauyin Karatun Ɗaliban Jigawa A Khadija University Majia
Gidauniyar Malam Adamu Foundation (MAF) ta Alhaji Musa Adamu Majia mamallakin Jami’ar Khadija da ke Majia a Jihar Jigawa zata ɗau nauyin karatun ɗalibai masu ƙaramin ƙarfi a Khadija University Majia.
MAF ta tanadi ɗaukar nauyin karatun!-->!-->!-->…
Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Ɗaurin Shekaru 5 Kan Farouk Lawan
Kotun Ƙoli ta tabbatar da hukuncin ɗaurin shekaru biyar kan tsohon Ɗan Majalissar Wakilai, Farouk Lawan bisa kama shi da laifin karɓar cin hanci na dala 500,000 daga sanannen ɗan kasuwar nan Femi Otedola.
An dai binciki Farouk Lawan ne!-->!-->!-->…
Soja Na Samun Ƙasa Da Naira 50,000 A Wata – In Ji Babban Hafsan Sojojin Najeriya
Babban Hafsan Sojojin Najeriya, Janaral Christopher Musa ya bayyana cewar ana biyan sojojin Najeriya albashin naira 50,000 ne a kowanne wata, yayin da shi kansa da sauran sojoji ke samun naira 1,200 a matsayin alawuns na aiki a kowacce!-->…
PDP Ta Buƙaci INEC Ta Sanya Lokacin Gudanar Da Zaɓen Cike Guraben Ƴan Majalissu 25 Na Jihar Rivers
Jam’iyyar Peoples Democratic Party, PDP, ta yi kira Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa, INEC, da ta sanya ranar gudanar da sabon zaɓen cike guraben ƴan majalissun Jihar Rivers 25 da suka fice daga jam’iyyar suka koma jam’iyyar APC.
!-->!-->!-->…