Sign in
Sign in
Recover your password.
A password will be e-mailed to you.
Browsing Category
Gwamnati
DA ƊUMI-ƊUMI: Mai Magana Da Yawun Shugaba Tinubu, Ngelale Ya Tafi Hutun Sai Baba Ta Gani
Mai bai wa Shugaban Ƙasa Bola Tinubu Shawara kan Harkokin Yaɗa Labarai, Ajuri Ngelale, ya tafi hutun sai baba ta gani saboda rashin lafiya ba tare da shiri ba.
Ngelale ya bayyana cewa ya ɗauki wannan matakin ne bayan shawarwari da!-->!-->!-->…
Talauci A Najeriya Zai Zarce Hasashen Bankin Duniya Kwanan Nan Saboda Tsadar Man Fetur
Masana tattalin arziƙi sun yi gargaɗin cewa adadin ƴan Najeriya da ke ƙasa da layin talauci na iya zarce hasashen Bankin Duniya na mutane miliyan 104, sakamakon hauhawar farashin fetur da matsalolin samar da abinci da ƙasar ke fuskanta.
!-->!-->!-->…
BASHIN KARATU: Mun Fara Jin Alat Na Kuɗin Rijistar Ɗalibanmu – Shugaban Wata Makaranta
Shugaban makarantar Moshood Abiola Polytechnic, MAPOLY, da ke Abeokuta, Dr. Adeoye Odedeji, ya ce ɗaliban makarantar sun fara samun kuɗi na bashin karatun da suka nema.
Odedeji ya bayyana hakan ne ranar Juma’a a Abeokuta yayin rantsar!-->!-->!-->…
Ku Kare Kanku Daga Ƴanta’add, Gwamnan Katsina Ya Shawarci Ƴan Jiharsa
Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umar Radda, ya yi kira ga al’ummar jihar da su ɗauki matakan kariya don kare kansu daga hare-haren ƴanbindiga da ke addabar jihar.
Ya bayyana hakan ne a taron dandalin tattaunawa da aka gudanar mai taken:!-->!-->!-->…
Mutane 13, 346 Aka Kashe, Aka Sace 9,207 A Watanni 16 Na Mulkin Tinubu, In Ji Wani Rahoto
Tun bayan rantsar da Shugaba Bola Tinubu a ranar 29 ga watan Mayu, 2023, Najeriya ta fuskanci ƙaruwar tashin hankali, inda aka kashe mutane 13,346 aka kuma yi garkuwa da 9,207 a fadin kasar.
Wannan ƙaruwar tashin hankalin da ta shafi!-->!-->!-->…
Tinubu Na Ƙoƙarin Ɗabbaƙa Cigaban Ababen More Rayuwa Irin Na China A Najeriya
Shugaban kasa Bola Tinubu ya nuna kudirinsa na kwaikwayon cigaban kasar Sin a fannin ababen more rayuwa a Najeriya bayan ziyararsa zuwa kasar.
Ya bayyana hakan ne yayin ganawa da kungiyar 'yan Najeriya mazauna kasar Sin (NIDO China) da!-->!-->!-->…
Ba Mu Hana Ƴan Ƙasa Da Shekara 18 Rubuta WASSCE Da NECO Ba – Ministan Ilimi
Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya ta fayyace cewa ba ta dakatar da ɗaliban da ba su kai shekara 18 ba daga rubuta jarrabawar WASSCE ko NECO.
Ƙaramin Ministan Ilimi, Dr. Yusuf Sununu ne ya bayyana haka a Abuja yayin da yake amsa tambayoyi daga!-->!-->!-->…
A Shirye Nake Na Ɗau Duk Wasu Tsauraran Matakai Don Ciyar Da Najeriya Gaba – Tinubu
Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya bayyana cewa yana shirye ya ɗauki tsauraran matakai don ciyar da ƙasa gaba, duk da cewa ba koyaushe ake samun haɗin kan ƴan ƙasa kan batutuwan ba.
Tinubu ya yi wannan bayani ne a Beijing lokacin da yake!-->!-->!-->…
Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 152, Sun Kama 109, Sun Ceto Mutane 91
Sojoji sun kashe ƴan ta’adda 152, sun kama 109, sun ceto mutane 91 da aka yi garkuwa da su, a yayin da suke yaƙi da matsalar tsaro a fadin kasar nan cikin makon da ya gabata.
Sojojin sun kai hari kan sansanonin wasu manyan shugabannin!-->!-->!-->…
Kukah Ya Roƙi Shugabannin APC Da Su Janye Ƙarin Kuɗin Man Fetur A Kan Ƴan Najeriya
Bishop Mathew Hassan Kukah na Cocin Katolika ta Sokoto ya yi kira ga shugabannin jam’iyyar APC mai mulki da su rage farashin man fetur da ake sayarwa, yana mai cewa ƴan Najeriya na cikin halin yunwa.
Ya yi wannan jawabi ne a yau Juma'a!-->!-->!-->…
Ƴanta’adda Sun Mayar Mu Bayi, Suna Sa Mu Aiki A Gonakinsu – Ƴan Jihar Niger
Mutanen da ke zaune a wasu garuruwa da ke fama da matsalar tsaro a Ƙaramar Hukumar Shiroro da ke Jihar Neja, sun koka cewa ƴan ta’adda da ƴan bindiga na bautar da su wajen aikin gona a gonakin su.
An gano cewar, shugaban wata ƙungiyar!-->!-->!-->…
CAC Ta Gargaɗi Masu POS Da Ba Su Yi Rijista Ba, Ta Ce Ana Iya Rufe Asusunsu
Hukumar CAC ta gargadi masu gudanar da kasuwancin POS da ba su yi rijista ba yayin da wa’adin da aka ba su ya ƙare.
Tun a baya dai aka sanar da su wa’adin yin rijista da aka ayyana tun ranar 7 ga Yuli, 2024, kuma wa’adin ya cika a ranar!-->!-->!-->…
Iya Masu NIN Number Ne Zasu Mori Sayen Shinkafa Kan Farashin Naira 40,000
Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa kawai mutanen da ke da Lambar Shaidar Ɗan Ƙasa ta NIN ne za su samu damar sayen buhun shinkafa mai nauyin 50kg a farashin N40, 000 a matsayin wani bangare na tallafin abinci ga ƴan Najeriya.
Shugaban!-->!-->!-->…
Sai Ranar 15 Ga Satumba Man Ɗangote Zai Shiga Gidajen Man Najeriya – NNPC
Matatar Man Fetur ta Dangote zata fara cika kasuwar man fetur da mai daga ranar 15 ga Satumba, 2024, kamar yanda Kamfanin Man Fetur na Najeriya, NNPCL, ya sanar.
Sanarwar da Olufemi Soneye, Jami’in Hulda da Jama’a na NNPCL ya!-->!-->!-->…
Gamayyar Marassa Rinjaye A Majalissar Wakilai Ta Nemi A Gaggauta Janye Ƙarin Farashin Mai
Gamayyar marassa rinjaye a Majalisar Wakilai ta nemi a gaggauta janye ƙarin farashin man fetur da aka ƙara kwanan nan, saboda hakan zai ƙara wa 'yan Najeriya wahala.
Sanarwar da shugabansu Kingsley Chinda ya fitar ta ce wannan ƙarin!-->!-->!-->…
YANZU-YANZU: Ɗaliban Najeriya Zasu Rufe Duk Manyan Birane, Yayin Da NANS Ta Ba Da Sanarwar Fara…
Kungiyar Daliban Najeriya, NANS, ta fitar da sanarwar shirin rufe dukkan manyan biranen Najeriya, daga ranar 15 ga Satumba, 2024.
Zanga-zangar na da nufin nuna rashin amincewa da ƙarin farashin man fetur da kuma zargin rashin kwarewa da!-->!-->!-->…
Adadin Karɓar Rigakafi Ya Ƙaru Zuwa Kashi 49% Cikin Shekara Biyar A Jigawa – Hukuma
Daraktan Kiwon Lafiya a Matakin Farko na Jihar Jigawa, Dr. Shehu Sambo, ya ce adadin rigakafi ya karu daga kashi bakwai cikin dari a shekarar 2016 zuwa kashi 49 cikin dari a shekarar 2021.
Sambo ya bayyana hakan ne yau Laraba a Dutse,!-->!-->!-->…
Gwamnatin Jigawa Za Ta Kafa Cibiyoyin Kula Da Ciwon Ƙoda Biyar A Jihar
Gwamnatin Jihar Jigawa ta shirya kafa cibiyoyin kula da ciwon ƙoda guda biyar a jihar, kamar yanda Kwamishinan Lafiya, Dr. Muhammed Kainuwa ya bayyana.
Kainuwa ya bayyana hakan ne a Dutse yayin buɗe taron karɓar takardun neman kwangilar!-->!-->!-->…
Yawan Wutar Lantarki Ya Kai Megawatt 5,313, Karo na Farko Cikin Shekaru 3 – Minista
Yawan wutar lantarki a Najeriya ya karu zuwa megawatt 5,313 a ranar Litinin da ta gabata, karo na farko cikin shekaru uku, a cewar Ma’aikatar Wutar Lantarki.
Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Bolaji Tunji, Mai ba da shawara ta!-->!-->!-->…
Fursunoni 3,590 Na Jiran Hukuncin Kisa A Najeriya – NCoS
Akalla fursunoni 3,590 ne da ke cikin gidajen gyaran hali a fadin Najeriya ke jiran hukuncin kisa, kamar yanda Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Najeriya (NCoS) ta bayyana.
Mai magana da yawun hukumar, Mataimakin ACC Abubakar Umar,!-->!-->!-->…