Sign in
Sign in
Recover your password.
A password will be e-mailed to you.
Browsing Category
Labarai
Sabbin labarai daga gida da waje cikin Hausa, tare da bayanai masu zurfi da gaskiya. Muna kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya, Arewa da sauran duniya cikin lokaci. Karanta takaitattun rahotanni, bincike da kwakkwaran bayani.
DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnatin Kano Ta Hana Private Schools Ƙarin Kuɗin Makaranta
Gwamnatin Kano ta tabbatar da dakatar da ƙarin kuɗin makaranta da makarantu masu zaman kansu na jihar ke ƙoƙarin yi.
Sannan gwamnatin ta umarci dukkan makarantun da su sabunta lasisinsu domin su dace da tsarin inganta ilimi na gwamnan!-->!-->!-->…
An Kashe Sojojin Nijar 17 A Iyakar Ƙasar Da Mali
An kashe sojojin Jamhuriyar 17 a jiya Talata a wani hari da ake zargin ƴan ta’adda ne suka kai musu a iyakar ƙasar ta yamma wadda ta haɗa ƙasar da Mali, in ji Ma’aikatar Tsaro ta ƙasar.
Ma’aikatar Tsaron ta ce, sojojin sun fuskanci!-->!-->!-->…
Ƴan Najeriya Na Nadamar Cin Zaɓen Tinubu Da APC, In Ji PDP
Jam’iyyar Peoples Democratic Party, PDP, reshen Jihar Ondo, a jiya Talata, ta bayyana matsayarta kan yanayin wahalar rayuwar da ƴan Najeriya ke sha, wadda jam’iyyar ta bayyana a matsayin abun da aka ƙaƙabawa ƴan Najeriya ta hanyar tallata!-->…
Ƴansanda Sun Kama Ɓarayin Wayar Lantarki, Shanu, Awaki Da Ƴan-Fashi A Jigawa
Jami’an ƴansanda na Rundunar Ƴansanda ta Jihar Jigawa sun kama wasu da ake zargin ƙwararrun ɓarayin shanu da awaki ne a garin Maigatari.
Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar, DSP Shiisu Adam ne ya bayyana hakan lokacin da yake jawabi ga!-->!-->!-->…
HOTUNA: Kashifu Inuwa Ya Karɓi Baƙuncin Shugabannin Google Kan Bunƙasa Fasahar Zamani Ga Matasa
Babban Daraktan Hukumar Bunƙasa Fasahar Zamani da Sadarwa, NITDA, Malam Kashifu Inuwa Abdullahi ya karbi baƙuncin tawaga ƙarƙashin jagorancin Olu,ide Balogun, Daraktan Google na Afirka ta Yamma daga kamfanin Google.
KARANTA WANNAN:!-->!-->!-->…
An Saka Ranaku, Gurare Da Lokutan Tantance Ƴan J-Teach Masu Digiri A Jigawa
Ma’aikatar Ilimi mai Zurfi, Kimiya da Fasaha ta Jihar Jigawa ta sanar da ranakun tantance waɗanda suka zana jarabawar neman aikin koyarwa na J-Teach a jihar.
Ma’aikatar ilimin ta rarraba ranakun gudanar da tantancewar zuwa yankunan!-->!-->!-->…
TSADAR MAI: Babu Wani Shirin Dawo Da Tallafin Mai A Najeriya, In Ji Fadar Shugaban Ƙasa
Babban Mai Temakawa Shugaban Ƙasa a Kan Harkokin Yaɗa Labari da Hulɗa da Jama’a. Tope Ajayi, ya ce, babu wani shirin da gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu take yi na dawo da tallafin man fetur.
Ajayi ya yi wannan bayani ne a yau!-->!-->!-->…
Wasu Da Ake Zargin Makiyaya Ne Sun Kai Hari Wata Makaranta, Sun Kashe Ango Da Amarya
Wani ango da amaryarsa, sabbin aure, sun rasa ransu a yayin da wasu da ake zargin makiyaya ne suka kai hari kan Makarantar Sikandire ta BECO Comprehensive da ke garin Kwi a Ƙaramar Hukumar Riyom ta Jihar Plateau.
Lamarin dai ya faru ne!-->!-->!-->…
Ana Matsawa Najeriya Kan Ta Amince Da Auren Jinsi
Cocin Angalican ta Najeriya ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta bijirewa kiraye-kirayen da Turawan Yamma ke mata na ta sake matsayinta kan auren jinsi a Najeriya.
Wannan dai na a cikin jawabin bayan taron da cocin ta saki bayan!-->!-->!-->…
Ƴanbindiga Sun Kashe Sojoji 13 Tare Da Harbo Jirgin Yaƙi A Jihar Neja
Ƴanbindiga sun mamaye mazaɓar Chukuba da ke Ƙaramar Hukumar Shiroro ta Jihar Neja, yayin da suka harbo jirgin yaƙi na sojoji tare da kashe matuƙinsa.
Shugaban Ƙungiyar Matasa ta Shiroro, Sani Koki wanda yai magana da ƴanjaridu ta waya a!-->!-->!-->…
Masu HND Zasu Mallaki Shaidar Digiri A Shekara 1 A Sabon Shirin Gwamnati
Hukumar Kula da Ilimin Fasaha ta Ƙasa, NBTE, ta ƙaddamar da shirin yin karatu ta yanar gizo ga masu shaidar Babbar Diploma ta Ƙasa, HND, domin su mallaki shaidar kammala digiri a shekara ɗaya.
NBTE ta bayyana cewar, karatun na shekara!-->!-->!-->…
Masu Juyin Mulkin Nijar Zasu Yankewa Bazoum Hukuncin Cin Amanar Ƙasa
A ranar Lahadin da ta gabata ne da daddare, gwamnatin mulkin sojin Nijar ta yi iƙirarin yankewa tsohon shugaban ƙasar da ta tunɓukar, Mohammed Bazoum hukuncin cin amanar ƙasa.
Sojojin sun kuma kushe hukuncin shugabannin ƙasashen Afirka!-->!-->!-->…
Kwanannan Naira Zata Farfaɗo, Masu Dala Zasu Tafka Asara – CBN
Akwai ƙwararan alamu da ke nuni da cewar, Babban Bankin Najeriya, CBN, ya shirya domin ɗaukar matakan farfaɗo da darajar naira a ƴan kwanaki masu zuwa kaɗan.
Wannan ci gaba dai idan ya tabbata, ana sa ran zai jawo faɗuwar farashin dala!-->!-->!-->…
YANZU-YANZU: Jirgin Sojan Saman Najeriya Ya Yi Hatsari A Jihar Neja
Wani jirgin saman sojoji mallakin Rundunar Sojan Saman Najeriya, NAF, ya yi hatsari.
Jirgin dai ya tashi ne daga Kaduna yana kan hanyarsa ta zuwa Minna, babban birnin Jihar Neja lokacin da hatsarin ya faru.
Da yake tabbatar da!-->!-->!-->!-->!-->…
DA ƊUMI-ƊUMI: NLC Ta Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki Matuƙar Aka Ƙara Kuɗin Mai
Ƙungiyar Ƙwadago, NLC, ta yi barazanar tsunduma yajin aikin sai-baba-ta-gani a duk faɗin Najeriya matuƙar aka ƙara kuɗin man fetur daga naira 617 da ake siyarwa a yanzu.
Ƙungiyar ta bayyana yunƙurin ƙarin da take ji ana yi a matsayin!-->!-->!-->…
Mazaɓun Sanatoci 6 Da Ba Su Taɓa Yin Gwamna Ba Tun 1999
Binciken da DAILY TRUST ta yi ya nuna cewar akwai aƙalla mazaɓun sanatoci guda 6 a Arewacin Najeriya da ba su taɓa fitar da gwamna a jihohinsu ba tun dawowar mulkin demokaraɗiyya a shekarar 1999.
Mazaɓun sune, Mazaɓar Benue ta Kudu,!-->!-->!-->…
BUK Ta Samarwa Ɗalibanta Aikin Da Zasu Na Samun Naira 15,000 Duk Wata
Shugaban Jami’ar Bayero da ke Kano, BUK, Farfesa Sagir Adamu Abbas ya bayyana cewa, jami’ar ta ɓullo da tsarin samar da aikin yi ga ɗalibai.
Farfesa Sagir ya ce, jami’ar ta ɗauki ɗalibai wani aiki da zasu na yi mata ana biyansu naira!-->!-->!-->…
Gwamnatin Kano Ta Soke Lasisin Makarantu Masu Zaman Kansu
Gwamnatin Jihar Kano ta soke lasisin dukkan makarantu masu zaman kansu da ke faɗin jihar.
Gwamnatin ta ɗauki wannan mataki ne a ranar Asabar da ta gabata, a lokacin zaman tattaunawa tsakaninta da masu makarantu masu zaman kansu a jihar.!-->!-->!-->…
Kwanannan Za A Koma Siyar Da Litar Fetur Naira 720 Saboda Faɗuwar Darajar Naira
Masu siyar da mai sun nuna cewar farshin man fetur zai tashi daga yanda yake a yanzu ya koma tsakanin naira 680 zuwa 720 a kwanaki masu zuwa matuƙar aka ci gaba da canja dala a kan naira 910 zuwa 950 a guraren canjin kuɗaɗe.
Su kuma!-->!-->!-->…
RANAR MATASA: Ka Yunƙura Ka Fi Ƙarfin Masu Bautar Da Kai Ya Kai Matashi
Daga: Comrade Musa Isma’il Birnin Kudu
Ni bana murna da ranar matasa don ba mu san kanmu ba har yanzu, mun biyewa kwaɗayi, maula, tumasanci da shirmen azzaluman ƴan siyasar da rayuwarsu ta kusan ƙarewa suna juya mana tunani suna ruguza!-->!-->!-->…