Sign in
Sign in
Recover your password.
A password will be e-mailed to you.
Browsing Category
Tsaro
Rahotanni kan tsaro: rundunonin tsaro, dokoki, dabaru da wayar da kai. Muna tattauna hanyoyin kare al’umma da inganta zaman lafiya. Rahotanni kan ’yan sandan Najeriya, sojoji, da sauran hukumomin tsaro.
Ƴan-ta’adda 41 Ne Suka Mutu A Faɗan Da Ya Ɓarke Tsakanin Boko Haram Da ISWAP A Borno
Mayaƙan Boko Haram da na ISWAP a ƙalla 41 aka kashe bayan ɓarkewar faɗa tsakanin ƴan ƙungiyoyin a jiya Laraba a Jihar Borno.
Bayanai sun tabbatar da cewar, mayaƙan ISWAP waɗanda suka je wajen faɗan a kan ƙananan jiragen ruwa, sun!-->!-->!-->…
Dubunnan Mutanen Da Suka Mutu A Dalilin Faɗan Manoma da Makiyaya
Malamai a Sashin Koyar da Kimiyyar Siyasa na Jami’ar Abuja sun koka kan irin rayuka da dukiyoyin da aka rasa a sanadiyyar faɗan manoma da makiyaya a jihohin Benue da Plateau.
Malaman sun bayyana rashin ƙoƙari daga ɓangaren gwamnati!-->!-->!-->…
Wani Mutum Ɗan Shekara 50 Ya Kashe Agolan Gidansa A Jigawa
Rundunar ƴansandan Jihar Jigawa ta kama wani mutum ɗan shekara 50 mai suna Ibrahim Adamu da gangancin yin amfani da abu mai kaifi wajen yanka agolan gidansa ɗan shekara huɗu a duniya.
Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar Ƴansandan Jihar!-->!-->!-->…
Wani Tsoho Ɗan Shekara 84 Ya Kashe Matarsa Saboda Ta Ƙi Kwanciya Da Shi
Wani tsoho ɗan shekara 84 mai ƴaƴa 7 mai suna Gabriel Uhuwa ɗan Jihar Edo ya faɗa komar ƴansanda saboda zarginsa da ake da kashe matarsa saboda ta ƙi yarda ta kwanta da shi.
Ƴansandan ne suka tabbatar da kama tsohon a jiya Laraba,!-->!-->!-->…
An Kashe Sojojin Nijar 17 A Iyakar Ƙasar Da Mali
An kashe sojojin Jamhuriyar 17 a jiya Talata a wani hari da ake zargin ƴan ta’adda ne suka kai musu a iyakar ƙasar ta yamma wadda ta haɗa ƙasar da Mali, in ji Ma’aikatar Tsaro ta ƙasar.
Ma’aikatar Tsaron ta ce, sojojin sun fuskanci!-->!-->!-->…
Ƴansanda Sun Kama Ɓarayin Wayar Lantarki, Shanu, Awaki Da Ƴan-Fashi A Jigawa
Jami’an ƴansanda na Rundunar Ƴansanda ta Jihar Jigawa sun kama wasu da ake zargin ƙwararrun ɓarayin shanu da awaki ne a garin Maigatari.
Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar, DSP Shiisu Adam ne ya bayyana hakan lokacin da yake jawabi ga!-->!-->!-->…
Wasu Da Ake Zargin Makiyaya Ne Sun Kai Hari Wata Makaranta, Sun Kashe Ango Da Amarya
Wani ango da amaryarsa, sabbin aure, sun rasa ransu a yayin da wasu da ake zargin makiyaya ne suka kai hari kan Makarantar Sikandire ta BECO Comprehensive da ke garin Kwi a Ƙaramar Hukumar Riyom ta Jihar Plateau.
Lamarin dai ya faru ne!-->!-->!-->…
Ƴanbindiga Sun Kashe Sojoji 13 Tare Da Harbo Jirgin Yaƙi A Jihar Neja
Ƴanbindiga sun mamaye mazaɓar Chukuba da ke Ƙaramar Hukumar Shiroro ta Jihar Neja, yayin da suka harbo jirgin yaƙi na sojoji tare da kashe matuƙinsa.
Shugaban Ƙungiyar Matasa ta Shiroro, Sani Koki wanda yai magana da ƴanjaridu ta waya a!-->!-->!-->…
Masu Juyin Mulkin Nijar Zasu Yankewa Bazoum Hukuncin Cin Amanar Ƙasa
A ranar Lahadin da ta gabata ne da daddare, gwamnatin mulkin sojin Nijar ta yi iƙirarin yankewa tsohon shugaban ƙasar da ta tunɓukar, Mohammed Bazoum hukuncin cin amanar ƙasa.
Sojojin sun kuma kushe hukuncin shugabannin ƙasashen Afirka!-->!-->!-->…
YANZU-YANZU: Jirgin Sojan Saman Najeriya Ya Yi Hatsari A Jihar Neja
Wani jirgin saman sojoji mallakin Rundunar Sojan Saman Najeriya, NAF, ya yi hatsari.
Jirgin dai ya tashi ne daga Kaduna yana kan hanyarsa ta zuwa Minna, babban birnin Jihar Neja lokacin da hatsarin ya faru.
Da yake tabbatar da!-->!-->!-->!-->!-->…
Gwamnatina Zata Magance Matsalar Tsaro A Najeriya – Shugaba Tinubu
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce, gwamnatinsa zata tanadi abubuwan da ake buƙata domin ƙara ƙarfin jami’an tsaro da samar musu da ƙarin walwala a sabon ƙudirinta na magance matsalar tsaro da sauran abubuwan da ke da alaƙa da shi a!-->…
An Yi Wa Wata Ma’aikaciyar Jiyya Kisan Gilla Ta Hanyar Cire Mata Mahaifa
Wani abun tashin hankali ya ruɗa mutane jiya a birnin Ibadan, bayan da aka tsinci gawar wata matashiyar ma’aikaciyar jiyya mai suna Omoniyi Boluwatife.
Masu aikata aika-aikar, waɗanda har yanzu ba a kai ga gane su ba, sun yi wa Omoniyi!-->!-->!-->…
‘Tana Kirana Ne Kaɗai Idan Tana Buƙatar Kuɗi,’ In Ji Wanda Yai Wa Budurwarsa Kisan Gilla
Wani matashi ɗan shekara 45 mai suna Bankole Oginni, wanda ƴansanda suka kama a Jihar Ondo bisa zargin kashe tsohuwar budurwarsa, ya bayyana dalilan da suka sa ya aikata aika-aikar.
Wanda ake zargin dai ya aikata laifin ne a gidansa da!-->!-->!-->…
Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 3, Sun Ƙwato Makamai A Kaduna
Rundunar sojojin Najeriya ta ce dakarunta da ke 1 Division sun kashe ƴan bindiga uku tare da ƙwato makamai da sauran abubuwa a Ƙaramar Hukumar Chikun ta Jihar Kaduna.
A wata sanarwa da Musa Yahaya, mai riƙon Mataimakin Darakta kan Hulɗa!-->!-->!-->…
JUYIN MULKI: Sojoji Zasu Kare Demokaraɗiyyar Najeriya Komai Matsalolinta – Shugaban Sojoji
Hafsan Hafsoshin Najeriya, Lieutenant General Taoreed Lagbaja, a jiya Asabar ya yi alƙawarin cewa, sojojin Najeriya zasu ci gaba da kare demokaraɗiyyar Najeriya komai matsalolin da take fuskanta.
Janar Lagbaja ya bayar da wannan!-->!-->!-->…
An Harbe Wani Mai Temakawa Sanata Har Lahira
Adeniyi Sanni da ke a matsayin babban mai temakawa sanatan Ogun ta Yamma, Solomon Adeola ya gamu da ajalinsa bayan harbinsa da akai lokacin yana kan hanyarsa ta zuwa gidansa da ke yankin Isheri a Jihar Lagos jiya Asabar.
A wani jawabin!-->!-->!-->…
Ƴansanda Sun Kama Ƙasurgumin Mai Garkuwa Da Mutane Da Wata Ƴar Leƙen Asirinsu A Zamfara
Rundunar ƴansandan Jihar Zamfara sun kama wani ƙasurgumin mai garkuwa da mutane mai suna Lawali Danhajiya, wanda ya ƙware a yin garkuwa da mutane a Gusau, babban birnin Jihar Zamfara.
Haka kuma ƴansandan sun samu nasarar kama wata ƴar!-->!-->!-->…
An Gurfanar Da Wani Mutum A Gaban Kotu Kan Kashe Ƙaninsa Ɗan Shekara 6
An kai wani mutum mai suna Kingsley Bassey gidan gyaran hali na Kirikiri bisa zargin kashe ƙaninsa ɗan shekara shida lokacin da yake cikin maye.
Ƴansanda ne suka gurfanar da mutamin ɗan shekara 23 a duniya a gaban Kotun Majistare ta!-->!-->!-->…
Masu Fyaɗe 5 Sun Yi Lalata Da Ƙaramar Yarinya A Jigawa, Ɗaya A Cikinsu Yana Da Ƙanjamau
Jami’an ƴansanda a Jigawa sun cafke mutane biyar da ake zargi da yin lalata da ƴar ƙaramar yarinya ƴar shekara 14, inda aka samu ɗaya a cikinsu ɗauke da ciwon ƙanjamau.
Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar Ƴansandan Jihar Jigawa, DSP!-->!-->!-->…
‘Zai Iya Zamewa Yaƙi,’ Burkina Faso Da Mali Sun Goyi Bayan Sojojin Nijar Sun Kuma Gargaɗi ECOWAS
Sojojin da ke mulki a Burkina Faso da Mali sun yi gargaɗi kan yunƙurin amfani da ƙarfin soji a kan sojojin da suka yi juyin mulki a Nijar, inda suka ce yin hakan tsokanar yaƙi ce a Afirka ta Yamma.
Gargaɗin wanda ya zo a wata sanarwar!-->!-->!-->…