Jaridar Hausa - Labaran Cigaban Alumma a Dukkan Fannoni

Mummunar Tsawa Ta Kashe Mutum 10 A Mozambique – Majalissar Dinkin Duniya

Majalisar Dinkin Duniya ta ce tsawa ta hallaka mutuane 10 bayan mamakon ruwan sama da kuma afkuwar wata mahaukaciyar guguwa a Mozambique.

Ofishin bayar da agaji na Majalissar Dinkin Duniya ta ƙara bayar da sanar cewa wasu mutum 11 sun mutu a Madagascar, inda gidaje sama da 3,300 suka lalace a ranar Lahadi lokacin da guguwar ta sake afkawa tsibirin.

WANI LABARIN: Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Jawo Mutuwar Mutane Da Dama A Kwande, Jihar Benue

Masu lura da yanayi, sun yi hasashen cewa mahaukaciyar guguwar za ta afkawa yankin tsakiya da kuma arewacin Mozambique a makon nan.

Guguwar ta kasance ɗaya daga cikin mafi daɗewa a cikin gwamman shekaru, inda ya tsallake ɗaukacin tekun Indiya daga bakin tekun Indonesia zuwa kudancin Afirka.

BBC